Train accidence in Lagos

Nigeria: Hatsarin jirgin kasa ya kashe mutane a Lagos
Sa'o'i 6 da suka wuce
Aika wannan shafi Facebook  Aika wannan shafi Twitter  Aika
Hakkin mallakar hotoGETTY IMAGES
Image caption
Najeriya dai tana kokarin farfado da layukan dogonta
A kalla mutum uku ne suka mutu bayan an yi hatsarin jirgin kasa a unguwar Agege da ke birnin Legas a kudancin Najeriya.
Shugaban sashen hulda da jama'a na hukumar jiragen kasa ta Najeriya da ke da hedikwata a Legas, Yakubu Mahmud, ya shaida wa BBC cewa lamarin ya faru ne a lokacin da wata motar tirela da take kokarin tsayawa ta daki jirgin kasan.
Jirgin dai ya taso ne daga yankin Ijoko zai tafi yankin Ido da suke cikin birnin Lagos din.
Jami'in ya ce wadanda suka rasa rayukansu suna cikin wadanda suka fado daga bakin kofar jirgin.
Wasu rahotanni na cewa akwai yiwuwar yawan wadanda suka mutu ya karu domin akwai mutane da dama da suka ji munanan raunuka.
Hakkin mallakar hotoGETTY IMAGES
Image caption
Ba kasafai ake samun hatsarin layin dogo a Najeriya ba
Ba a dai cika samun hatsarin jirgin kasa a Najeriya ba kamar su Indiya inda aka fi amfani da layin dogon.
Karanta karin wasu labaran:
Buhari na zawarcin sake tsayawa takara - Dr. Kari
An kashe yarinya a Nigeria don tsafi da sassan jikinta
Nigeria: An kashe dalibi kan zargin luwadi a Kano
Labarai masu alaka
Najeriya

Comments

Popular posts from this blog

ZAKAT AL - FITR

Buhari must support benue anti-grazing law

Today is silly questions asking day